Kasuwanci

Ƙarƙashin mulkin Tinubu Gwamnoni na samun ninkin kuɗaɗen da ake basu a baya

Informações:

Sinopsis

Shirin Kasuwa Akai Miki Dole tare da Ahmed Abba a wannan mako ya dubi batun ƙarin da aka samu a rabon arzikin ƙasa na wata-wata da gwamnatin Najeriya ke yi tsakaninta da jihohi da ƙananan hukumomin ƙasar, inda alƙaluma su ka nuna yadda wannan kaso ya ƙaru da ninkin abin da aka saba rabawa a baya, tun bayan zuwan wannan gwamnati ta shugaba Bola Tinubu a shekarar 2023. Ɓangararorin gwamnatoci uku a Najeriya, wato ta tarayya da ta jihohi da kuma ƙananan hukumomi sun raba kaso mafi yawa a tarihin rabon tattalin arzikin ƙasa na wata wata wanda ya kai sama da Naira Tiriliyan 2 da biliyan 200 a watan Agustan da ya gabata.... Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.