Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyi kan matakin Ghana na kama masu bace-barace

Informações:

Sinopsis

Matsalar barace-barace a kan titunan manyan birane a Yammavin Afirka sai daɗa yin ƙamari take, to sai dai bisa ga dukan alamu mahukunta a ƙasar Ghana sun ƙuduri aniyar kawo ƙarshen wannan ɗabi’a. Domin a cikin makon jiya, jami’an tsaro sun cafke mabarata sama da dubu biyu a birnin Accra kawai, kuma yawancinsu ƴan asalin ƙasashen Najeriya, Nijar, Burkina Faso da Mali ne.Shin ko akwai dalilan da za su sa jama’a su mayar da bara a matsayin sana’a?Ko waɗanne matakai ya kamata a ɗauka domin kawo ƙarshen wannan ɗabi’a ta bara?Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.