Bakonmu A Yau

Tattaunawa da Honourable Siraj Imam Ibrahim kan ambaliyar ruwan Kano

Informações:

Sinopsis

A ƙarshen makon da ya gabata aka samu ambaliyar ruwan sama a sassan birnin Kano, a dai dai lokacin da damina ta fara kankama a jihar. Wannan matsalar ta haifar da matsaloli ga mazauna da kuma baƙin da ke zuwa birnin. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban ƙaramar hukumar Dala, Hon Siraj Ibrahim Imam, Kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.   Ku latsa alamar sauti son sauraron cikakkiyar Hirar.