Sinopsis
A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.
Episodios
-
Dr. Harbau: Yadda ma'aikata za su nema wa kansu mafita
01/05/2025 Duración: 03minYau ɗaya ga watan Mayu take ranar Ma’aikata ta Duniya, ranar da ake duba gudummawa da sadaukarwar ma’aikata ga al’umma. A kan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Dokta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziki a jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke jihar Kano a Najeriya, wanda ya duba yadda wannan rana ta riski ma’aikata, tare da shawartar su a kan nema wa kansu mafita a yanayi da albashi ba zai wadata ba wajen tafiyar da rayuwa mai inganci.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakakkiyar hirarsu
-
Morocco ta baiwa ƙasashen AES damar yin amfani da tashar ruwanta
30/04/2025 Duración: 03minA daidai lokacin da rikici tsakanin Mali da Algeria ke cigaba da ruruwa, Sarkin Morocco Mohammed VI ya gayyaci ministocin harkokin wajen ƙasashen Burkina Faso,Mali da kuma jamhuriya Nijar a fadarsa da ke birnin Rabat domin basu damar yin fanin da tashar ruwanta na Atlantic wajan jigilar kayakinsu.Ziyarar tasu dai na zuwa ne bayan da alaƙa tsakanin ƙasashen AES da Algeria, wacce ke zama babbar abokiyar hamayyar Morocco ta yi tsami. Latsa alamar sauti domin suraron karin bayani.....
-
Tattaunawa da Farfesa Tukur Abdulkadir kan cikar Trump kwanaki 100 a mulki
29/04/2025 Duración: 03minYau shugaban Amurka Donald Trump le cika kwanaki 100 a karagar mulkin ƙasar, tun bayan rantsar da shi a ranar 20 ga watan Janairun shekarar nan. A tsawon wannan lokaci, shugaban na Amurka ya ɗauki mabanbantan matakai da suak girgiza sassan duniya.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Tukur Abdulkadir na Jami'ar Kaduna, don jin yadda masana ke kallon salon kamun ludayin Donald Trump ga kuma tattaunawarsu.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar..
-
Malam Isa Sanusi kan kisan fararen hula a jihar Zamfara
28/04/2025 Duración: 03minKungiyar Amnesty International ta tabbatar da mutuwar mutane 26 sakamakon harin ƴan bindiga a wurin hakar zinaren da ke jihar Zamfara. Daraktan ƙungiyar a Najeriya, Malam Isa Sanusi ne ya tabbatar da haka a tatatunawar da suka yi da Bashir Ibrahim Idris. Ku latsa alamar sautin don sauraron cikakkiyar tattaunawar tasu...........
-
Dalilin da ya sa ƴan adawar Najeriya ke sauya sheƙa zuwa APC
25/04/2025 Duración: 03min‘Yan adawa a Najeriya sun zargi gwamnatin ƙasar ta jam’iyyar APC da yi musu rinto ta hanyar amfani da ƙarfin tattalin arziƙin ƙasa da ke hannunta da kuma wasu dabaru wajen sanya jiga-jigai daga ɓangaren su ‘yan adawar sauya sheka zuwa ga jam’iyya mai mulki. Wannan lamari ya maido da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya a kan dalilan da suke haddasa yawaitar sauyin shekar ‘yan siyasa daga ɓangaren adawa zuwa gwamnati.Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Kamilu Sani Fagge na jami’ar Bayero a Najeriya.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyarsu
-
Farfesa Sadiq: Sabon nau'in cutar Polio ya karaɗe wasu jihohin Najeriya
24/04/2025 Duración: 03minAsusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF, ya ce an samu ɓullar sabon nau’in cutar Polio a ƙananan hukumomi 18 da ke wasu jihohin Najeriya 9 ciki har da Kano. Rahoton ya ce zuwa yanzu an samu rahotanni daban daban aƙalla 18 kan ɓullar sabon nau’in cutar ta Shan Inna, kuma an tattara bayanan ne a cikin watanni uku da suka gabata zuwa yanzu.Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Sadiq Isa Abubakar, shugaban cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa na asibitin Malam Aminu Kano da kuma jami'ar Bayero.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
-
Wasu yankunan Zamfara ba sa samun sauƙi duk da biyan 'yan bindiga da suke yi
23/04/2025 Duración: 03minMazauna ƙauyuka da dama a wasu yankunan jihar Zamfara, ciki har da yankin Gusau ta Gabas, na rayuwa cikin tsananin fargabar fuskantar hare-haren ‘yan bindiga, muddin suka gaza biyan miliyoyin Nairar da ‘yan ta’addan ke tilasta musu bayar wa a matsayin musayar barinsu su zauna lafiya.Yayin ƙarin bayani a kan halin da suke ciki, da kuma ƙauyukan da ke cikin tashin hankalin, wani mazaunin ɗaya daga cikin yankunan, ya ce biyan maƙudan kuɗaɗen da suke yi ba ya kawar da barazanar da suke ciki.
-
Farfesa Kamilu Sani Fagge kan daina tallafa wa rundunonin wanzar da zaman lafiya
22/04/2025 Duración: 04minGwamnatin shugaba Donald Trump ta gabatar da ƙudurin daina ba da tallafi ga rundunonin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya, saboda gazawar da ta ce rundunonin na yi a ƙasashen Mali da Lebanon da kuma Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo.Amurka ce dai ke kan gaba wajen tallafa wa ayyukan wanzar da zaman lafiyar a sassan Duniya, inda take samar da kusan kaso 27 cikin 100 na kasafin da ake buƙata.akan haka ne, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Farfesa Kamilu Sani Fagge.
-
Reverand Dayyu kan bikin Easter ta bana
21/04/2025 Duración: 03minYanzu haka ana ci gaba da gudanar da bukukuwan Easter, waɗanda ke matsayin tunawa da ranar da aka gicciye Yesu Almasihu da kuma tashinsa bayan kwanaki uku. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Reverand Andrew Dayyu, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da abin da ake nufi da Easter da kuma muhimmancinta ga mabiyar addinin Kirista. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar zantawarsu.............
-
Kan dalilan da ke sanya ƴan Najeriya faɗawa hannun ƴan damfara ta hanyar kuɗaɗen internet
17/04/2025 Duración: 03minDubban ‘yan Najeriya ne a cikin makon nan suka shiga cikin tashin hankali, sakamakon hasarar sama da Naira Tiriliyan 1 da suka tafka, a dalilin rushewar shafin CBEX, wanda ke hada-hadar kuɗaɗen Intanet. Shafin, ya ja hankalin mutane ne ta hanyar yi musu alƙawarin kason ribar 100 bisa 100 akan dukkanin adadin kuɗin da suka sanya cikinsa da zarar an cika kwanaki 30. Sai dai bayan ɗaukar wani ɗan lokaci, shafin tare da wakilansa da ke Najeriya suka yi layar zana.Kan wannan lamari, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Sagir Muhd mataimakin shugaban ƙungiyar ƙwararru kan na’ura mai ƙwaƙwalwa ta Najeriya......Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar
-
Tattaunawa da masani Umar Saleh Anka kan ambaliyar ruwa a jihohin Najeriya 30
15/04/2025 Duración: 03minGwamnatin Najeriya ta yi gargaɗin cewa jihohi 30 na ƙasar na fuskantar barazanar iftila’in ambaliyar ruwa yayin da daminar bana ta soma, kuma tuni ta fara shirin ƙaddamar da gangamin wayar da kan mutane game da illar ta da kuma hanyoyin rage kaifinta. To ko wace rawa hukumomi da al’umma za su taka dangane da rage mummanar illar da ambaliyar ke yi?Hauwa Halliru Gwangwazo ta tattauna da Umar Saleh Anka na ƙungiyar rajin kare muhalli a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar
-
Tattaunawa da Janjouna Ali Mahaman Sani kan zaɓen Gabon na gobe Asabar
11/04/2025 Duración: 03minA kasar Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajiberin zaɓen Shugaban ƙasar,wanda ya haɗa 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro.Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben.Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masani siyasar kasar ta Gabon da kewaye.Ga kuma yada zantawar tasu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
-
Abdoul Moumouni Abass kan rikicin Aljeriya da ƙasashen Ƙungiyar AES
10/04/2025 Duración: 03minRikici tsakanin Mali da Aljeriya na cigaba da ɗaukar saban salo, tun bayan da Aljeriya ta kakkaɓo wani jirgin sojin Mali mara matuƙi a kan iyakar ƙasashen biyu a farko makon jiya. Sai dai wani batu da ya baiwa kowa mamaki shi ne, yadda Nijar ta shigo cikin rikicin a matsayinta na mamba a ƙungiyar AES, wato saban kawance da ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar suka kafa bayan ficewrasu daga ECOWAS.Umar Sani ya tattauna da Abdoul Moumouni Abass mai sharhi kan siyasar ƙasa da ƙasa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
-
Tasirin harajin da Trump ya ɗorawa ƙasashen duniya a kan Afirka
08/04/2025 Duración: 03minA Laraba 9 ga watan Afrilu, sabon harajin da ya kama daga kashi 10 zuwa sama, da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba wa ƙasashen Afirka zai fara aiki, bayan da harajin da ya shafi sauran ƙasashe ya soma aiki a ranar 5 ga watan na Afrilu. Tun cikin makon jiya ne dai matakin na Trump ya soma tasiri a kasuwannin Turai da Asiya, a yayin da ƙasashen Afirka suka shiga zulumi dangane da makomarsu.Don jin tasirin da sabon harajin na Amurka zai yi a kan tattalin Arzikin arziƙin ƙasashen Afirka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Ƙasim Garba Kurfi.A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zanatawar.
-
Dakta AbdulHakim Garba Funtua akan harajin da Trump ya lafta wa duniya
03/04/2025 Duración: 03minƘasashe da dama ciki har da na Ƙungiyar EU, sun alwashin mayar da martanin ƙaƙaba wa kayayyakin Amurka haraji, kamar yadda shugaba Trump ya ƙaddamar da sabon tsarin karɓar harajin da ya ce ya shafi duniya baki ɗaya.Sabon harajin dai ya kama ne daga kashi 10 zuwa sama, wanda ya shafi hajoji daga kowace ƙasa, matakin da Trump matakin ya ce ya ɗauka ne don kare buƙatun al’ummar Amurka. Don jin yadda masana ke kallon sabon yaƙin kasuwancin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua.
-
Injiniya Safiya Sanusi: Kan sallamar Mele Kyari daga shugabancin NNPC a Najeriya
02/04/2025 Duración: 03minKamar yadda wataƙila aka ji cikin labarun duniyar da suka gabata, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi tankaɗe da rairaya a fannin man fetur ɗin ƙasar inda ya sallami shugaban kamfanin NNPCL malam Mele Kyari da shugaba da mambobin majalisar aminattu na kamfanin. Nan take ne kuma shugaba Tinubun ya maye gurbin manyan jami’an da ya sallama. Ko yaya ƙwararru ke kallon wannan sauyi? Wakilinmu a Abuja Muhd Sani Abubakar ya tattauna da Injiniya Safiyya Sanusi, ƙwararriya a fannin man fetur da Iskar Gas.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar
-
Alhaji Abubakar Maigandi kan tasirin daina sayarwa Ɗangote man fetur da Naira
02/04/2025 Duración: 03minGidajen man fetur a Najeriya na ci gaba da sauya farashi, bayan da matatar Dangote ta sanar da cewa yarjejeniyar da ke tsakaninta da NNPC wadda ke bayar da damar samun gurbataccen mai a farashin Naira ta kawo ƙarshe ba tare da an sabunta ta ba. Alhaji Abubakar Maigandi, shugaban ƙungiyar dillalan man fetur masu zaman kansu a Najeriya wato IPAM, ya ce tuni suka yi hasashen faruwar hakan bayan rugujewar waccan yarjejeniyar.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.
-
Barista Abba Hikima kan tsarin kiranye ga ƴan majalisu a dokokin Najeriya
27/03/2025 Duración: 03minA farkon makon nan, Hukumar Zaɓen Najeriya INEC, ta ce ba a kammala cika ƙa'idojin da kundin tsarin mulki ya gindaya ba, a kan tsarin kiranyen da ake ƙoƙarin yi wa Sanata Natasha mai wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya a zauren Majalisar Dattijai. INEC ta bayyana haka ne, bayan da ta fara nazari akan ƙorafe-ƙorafen da aka gabatar mata na nemn yi wa Sanata Natasha yankan ƙauna, wadda a kwanakin baya ta zargi shugaban Majalisar Dattawan Najeriyar Godswil Akpabio da cin zarafinta ta hanyar nemanta da lalata.Domin jin yadda tsarin na Kiranyen yake...Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Abba Hikima, ƙwararren lauya a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
-
Dr Auwal kan ɗauko hayar sojoji don horas da sojojin Najeriya wajen yaƙi da ta’addanci
26/03/2025 Duración: 03minGwamnatin Najeriya ta ɗauko hayar ƙwararrun sojoji daga wasu ƙasashen duniya, domin horas da sojojin ƙasar wajen yaƙi da ta’addanci, da kuma yin ƙundunbala wajen ceto mutanen da ‘yan ta’addan ke yin garkuwa da su. Ministan Tsaron Najeriya Badaru Abubakar ne ya sanar da matakin, a lokacin da yake ƙaddamar da aikin fara horas da kashin farko na sojojin Najeriyar a Kaduna. A kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Auwal Aliyu Abdullahi, mai magana da yawun Kwamitin musamman na kula da walwalar tsaffin sojoji a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu.............
-
Barista Al-Zubair kan matakin daina holin waɗanda ake zargi da ƴansanda ke yi
25/03/2025 Duración: 03minSufeta Janar na ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun, ya jaddada umarnin Antoni Janar na ƙasar, kan haramcin holin waɗanda ake zargi da aikata laifuka da jami’an tsaro ke yi ga manema labarai, ba tare da an hukuncin kotu ba. Ya ce a lokuta da dama jam’an tsaro basa iya gabatar da hujjoji kan zarge-zagen a gaban kotu, duk da cewa an nuna wa duniya fuskokinsu, lamarin da ya ce ya sabawa dokokin kare hakkin ɗan adam. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tsakanin Khamis Saleh da Barista Al-Zubair Abubakar........